Hausa
Surah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya count 60
وَالذَّارِيَاتِ ذَرْوًا
( 1 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 1 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 1](style/islamic/icons/mp3.png)
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
فَالْحَامِلَاتِ وِقْرًا
( 2 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 2 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 2](style/islamic/icons/mp3.png)
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
فَالْجَارِيَاتِ يُسْرًا
( 3 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 3 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 3](style/islamic/icons/mp3.png)
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
فَالْمُقَسِّمَاتِ أَمْرًا
( 4 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 4 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 4](style/islamic/icons/mp3.png)
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌ
( 5 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 5 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 5](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
وَإِنَّ الدِّينَ لَوَاقِعٌ
( 6 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 6 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 6](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْحُبُكِ
( 7 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 7 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 7](style/islamic/icons/mp3.png)
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
إِنَّكُمْ لَفِي قَوْلٍ مُّخْتَلِفٍ
( 8 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 8 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 8](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ
( 9 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 9 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 9](style/islamic/icons/mp3.png)
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
قُتِلَ الْخَرَّاصُونَ
( 10 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 10 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 10](style/islamic/icons/mp3.png)
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
الَّذِينَ هُمْ فِي غَمْرَةٍ سَاهُونَ
( 11 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 11 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 11](style/islamic/icons/mp3.png)
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
يَسْأَلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ الدِّينِ
( 12 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 12 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 12](style/islamic/icons/mp3.png)
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
يَوْمَ هُمْ عَلَى النَّارِ يُفْتَنُونَ
( 13 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 13 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 13](style/islamic/icons/mp3.png)
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
ذُوقُوا فِتْنَتَكُمْ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تَسْتَعْجِلُونَ
( 14 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 14 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 14](style/islamic/icons/mp3.png)
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
( 15 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 15 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 15](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
آخِذِينَ مَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ
( 16 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 16 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 16](style/islamic/icons/mp3.png)
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
كَانُوا قَلِيلًا مِّنَ اللَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ
( 17 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 17 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 17](style/islamic/icons/mp3.png)
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
وَبِالْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ
( 18 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 18 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 18](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
وَفِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ
( 19 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 19 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 19](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
وَفِي الْأَرْضِ آيَاتٌ لِّلْمُوقِنِينَ
( 20 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 20 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 20](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
وَفِي أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ
( 21 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 21 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 21](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
وَفِي السَّمَاءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ
( 22 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 22 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 22](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
فَوَرَبِّ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ إِنَّهُ لَحَقٌّ مِّثْلَ مَا أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ
( 23 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 23 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 23](style/islamic/icons/mp3.png)
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَ الْمُكْرَمِينَ
( 24 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 24 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 24](style/islamic/icons/mp3.png)
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
إِذْ دَخَلُوا عَلَيْهِ فَقَالُوا سَلَامًا ۖ قَالَ سَلَامٌ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ
( 25 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 25 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 25](style/islamic/icons/mp3.png)
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
فَرَاغَ إِلَىٰ أَهْلِهِ فَجَاءَ بِعِجْلٍ سَمِينٍ
( 26 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 26 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 26](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
فَقَرَّبَهُ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
( 27 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 27 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 27](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةً ۖ قَالُوا لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَامٍ عَلِيمٍ
( 28 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 28 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 28](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
فَأَقْبَلَتِ امْرَأَتُهُ فِي صَرَّةٍ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌ
( 29 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 29 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 29](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
قَالُوا كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُ هُوَ الْحَكِيمُ الْعَلِيمُ
( 30 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 30 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 30](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَ
( 31 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 31 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 31](style/islamic/icons/mp3.png)
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
قَالُوا إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ
( 32 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 32 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 32](style/islamic/icons/mp3.png)
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن طِينٍ
( 33 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 33 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 33](style/islamic/icons/mp3.png)
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ
( 34 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 34 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 34](style/islamic/icons/mp3.png)
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
( 35 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 35 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 35](style/islamic/icons/mp3.png)
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍ مِّنَ الْمُسْلِمِينَ
( 36 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 36 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 36](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
وَتَرَكْنَا فِيهَا آيَةً لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ الْعَذَابَ الْأَلِيمَ
( 37 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 37 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 37](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
وَفِي مُوسَىٰ إِذْ أَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ
( 38 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 38 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 38](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِ وَقَالَ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
( 39 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 39 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 39](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
فَأَخَذْنَاهُ وَجُنُودَهُ فَنَبَذْنَاهُمْ فِي الْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌ
( 40 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 40 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 40](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
وَفِي عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ الرِّيحَ الْعَقِيمَ
( 41 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 41 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 41](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
مَا تَذَرُ مِن شَيْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَالرَّمِيمِ
( 42 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 42 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 42](style/islamic/icons/mp3.png)
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
وَفِي ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا حَتَّىٰ حِينٍ
( 43 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 43 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 43](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
فَعَتَوْا عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ الصَّاعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ
( 44 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 44 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 44](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
فَمَا اسْتَطَاعُوا مِن قِيَامٍ وَمَا كَانُوا مُنتَصِرِينَ
( 45 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 45 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 45](style/islamic/icons/mp3.png)
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا قَوْمًا فَاسِقِينَ
( 46 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 46 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 46](style/islamic/icons/mp3.png)
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
وَالسَّمَاءَ بَنَيْنَاهَا بِأَيْدٍ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
( 47 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 47 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 47](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
وَالْأَرْضَ فَرَشْنَاهَا فَنِعْمَ الْمَاهِدُونَ
( 48 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 48 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 48](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
وَمِن كُلِّ شَيْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ
( 49 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 49 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 49](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
فَفِرُّوا إِلَى اللَّهِ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ
( 50 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 50 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 50](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
وَلَا تَجْعَلُوا مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ
( 51 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 51 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 51](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
كَذَٰلِكَ مَا أَتَى الَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
( 52 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 52 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 52](style/islamic/icons/mp3.png)
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
أَتَوَاصَوْا بِهِ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَ
( 53 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 53 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 53](style/islamic/icons/mp3.png)
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَا أَنتَ بِمَلُومٍ
( 54 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 54 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 54](style/islamic/icons/mp3.png)
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
وَذَكِّرْ فَإِنَّ الذِّكْرَىٰ تَنفَعُ الْمُؤْمِنِينَ
( 55 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 55 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 55](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ
( 56 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 56 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 56](style/islamic/icons/mp3.png)
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
مَا أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍ وَمَا أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ
( 57 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 57 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 57](style/islamic/icons/mp3.png)
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
إِنَّ اللَّهَ هُوَ الرَّزَّاقُ ذُو الْقُوَّةِ الْمَتِينُ
( 58 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 58 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 58](style/islamic/icons/mp3.png)
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا ذَنُوبًا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَابِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ
( 59 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 59 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 59](style/islamic/icons/mp3.png)
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
فَوَيْلٌ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا مِن يَوْمِهِمُ الَّذِي يُوعَدُونَ
( 60 ) ![Hausa - Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 60 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) - Aya 60](style/islamic/icons/mp3.png)
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.